IQNA

An Kashe Malaman Kur'ani Biyu A Burkina Faso

21:21 - August 15, 2017
Lambar Labari: 3481799
Banagren kasa da kasa, gwamnatin kasar Kuwait ta sanar da cewa, 'yan kasar guda biyu da aka kasha akasar Burkina Faso dukkaninsu malaman addinin muslunci ne.
Kamfanin dillancin labaran iqna ya habarta cewa, ya nakalto daga tashar Iram News cewa, mutanen biyu 'yan kasar Kuwait da aka kasha a harin Wagadugu su ne Walid Ali, wanda malamin jami'a ne mai koyar da ilmomin adini, kuma limamin babban masallacin kasar, sai kuma sheikh Fahad Alhusaini, wanda shi ma fitaccen malamin kur'ani ne a kasar ta Kuwait.

Wadannan malamai biyu sun yi tafiya zuwa kasar Burkina Faso ne domin gudanar da wani shiri na karatun kur'ani mai tsarki, da kuma ganawa da malamai addinin musluncia kasar, inda suka rasa rayukansu a jiya a lokacin musayar wuta da 'yan bindiga da suka yi garkuwa da jama'a a wani wurin cin abinci na Turkawa a birnin Wagadugu tun a daren Lahadin da ta gabata.

Sarkin Kuwait Sabah Jabir Ahmad sabah ya aike da jirgi na musamman domin dauko gawwakin mutanen biyu da nufin dawo da su gida domin yi musu janaza a cikin iyalansu.

Babbar jami'a mai kula da siyasar wajen tarayyar turai Federica Mogherini ta yi Allah wadai da kakakusar murya dangane da harin na Burkina Faso, tare da bayyana hakan a matsayin aiki na dabbanci.

Mutane 18 ne dai suka rasa rayukansu sakamakon harin, da suka hada da 'yan kasar ta Burkina faso da kuma wasu 'yan kasashen ketare.

3630570

دو مبلغ قرآنی کویت در بورکینافاسو کشته شدند + عکس
دو مبلغ قرآنی کویت در بورکینافاسو کشته شدند + عکس
دو مبلغ قرآنی کویت در بورکینافاسو کشته شدند + عکس
دو مبلغ قرآنی کویت در بورکینافاسو کشته شدند + عکس
دو مبلغ قرآنی کویت در بورکینافاسو کشته شدند + عکس
دو مبلغ قرآنی کویت در بورکینافاسو کشته شدند + عکس


captcha