IQNA

Gwamnatin Najeriya Na Bayar Da Horon Wayar Da Kai Ga 'Yan Boko Haram

21:23 - August 15, 2017
Lambar Labari: 3481800
Bangaren kasa da kasa, gwamnatin na ci gaba da aiwatar da shirin da ta fara na bayar da horo ga 'yan kungiyar Boko Haram da ake tsare da su a gidajen kaso kan koyarwar muslunci dangane da zaman lafiya.
Kamfanin dillancin labaran iqna ya habarta cewa, ya nakalto daga shafin plenglish cewa, majiyoyin gwamnatin Najeriya sun bayyana wanann shiri da cewa yana da matukar muhimmanci da kuma tasiri ga wadanda ake tsare da su daga cikin mayakan Boko Haram.

Malaman addinin muslunci da kuma masana kan halayyar dan adam ne suke jagorantar shiri, tare da saka ajujuwa na koyarwa da kuam wayar da kai a kan hakikanin koyarwar muslunci kan muhimamncin zaman lafiya da kaunar juna da kuma taimakekeniya a tsakanin al'umma.

Masana halayyar dan adam da ke cikin shirin suna ganawa da iyalan wadanda hare-haren Boko Haram suka rutsa da su, domin kwantar musu da hankali da kuma basu shawarwari, musamman ma wadanda lamarin ya cutar da lafiyarsu ko hankalinsu.

Najeriya ta ce za ta fadada wannan shirin tare da sauran makwabtanta da suke fama da irin wannan matsala ta hare-haren Boko Harama cikin kasashensu.

3630597


captcha