Kamfanin dillancin labaran iqna ya bayar da rahoton cewa, ya nakalto daga shafin yada labarai Christian Daily cewa, an gudanar da wannan zaman taro ne tare da halartar wakilan musulmi da kuma na kiristoci a wannan majami’a.
Babbar manufar taron dai ita ce kara samun fahimtar juna a tsakanin bangarorin biyu, da kuma yin Allah wadai da ayyukan da wasu suke aikatawa na cin zarafi ga musulmi sakamakon ayyukan ta’addanci da wasu suke aikatawa a da sunan muslunci.
Dukkanin bangarorin biyu sun yi Allah wadai da ayyukan ta’addanci daga kowane bangare suka fito, tare da jaddada cewa musulunci da kiristanci ba addinai na ta’addaci ba, addinai ne na zaman lafiya da fahimtar juna a tsakanin al’ummomi.