IQNA

Ana Zargin Mahukuntan Bahrain Da Cin Zarafin ‘Yan Adam

23:31 - July 01, 2018
Lambar Labari: 3482801
Bangaren kasa da kasa, kungiyar kare hakkin bil'adama ta kasar Bahrain ta fitar da rahoto a jiya asabar da a ciki ta zargi mahukuntan kasar da take hakkin bil'adama

 

Kamfanin dillancin labaran iqna rahoton ya nakalto cewa a cikin watan Mayu na wannan shekarar kadai an sami wuraren dubu daya da dari biyu da sabain da biyu da aka take hakkin dan adam a cikin kasar.

Rahoton ya kuma ci gaba da cewa; Take hakkin bil'ada da aka tabbatar da faruwarsa ya kunshi kai wa gidajen mutane hari, shari'ar da babu adalci a cikinta, murkushe masu gangamin ruwan sanyi.

Bugu da kari rahoton ya ambaci takurawa mutane masu kai da komowa akan tituna ta hanyar kafa shinge a matsayin wani sashe na take hakkin bil'adama. Har ila yau an zargi maukuntan kasar da hana yin sallar juma'a da kuma azabar da fursunoni.

A cikin wannan shekara ta dubu biyu da sha takwas kadai an yi wa mutane dari bakawai da bakwai shari'ar da babu adalci a cikinta, kamar yadda aka kwacewa mutane dari da talatin da biyar hakkin zama 'yan kasa, kamar yadda rahoton ya ambata.

Tun a watan febrairu na dubu biyu da sha daya  ne al'ummar Bahrain suka yunukura da zummar kawo gyara a salon siyasar kasar.

 

3726340

 

 

 

 

 

captcha