Kamfanin dillancin labaran iqna ya habarta cewa, wasu daga cikin ‘yan majalisar haramtacciyar kasar Isra’ila sun kutsa kai a cikin masallacin quds mai alfarma da nufin keta alfarmar wannan wuri mai albarka.
Yahudawan sun shiga cikin masallacin ne tare da kariya daga daruruwan jami’an tsaron Isra’ila.
A cikin ‘yan kawanakin nan dai yahudawa suna yawan shiga cikin wannan masallaci mai alfarma domin tsonakar al’ummar musulmi.
Tun bayan da shugaban Amurka ya ayyana birnin Quds a matsayin babban birnin yahudawan Israila a hukumance, yahudawan suke ta kara cin karensu babau babbaka a kan musulmi da wurare masu tsarki a wannan birni.