Kamfanin dillancin labaran iqna ya habarta cewa, majami’oin mabiya addinin kirista akasar Zimbabwe za su gudanar da jerin gwanon lumana a birnin Harare domin neman a yi zaben 2018 cikin cikin sulhu da kwanciyar hankali.
Manyan majami’oin birnin Harare fadar mulkin kasar ta Zimbabwe ne suka shirya wannan gangami da jeri gwano, da nufin ganin sun ja hankulan jama’ar kasar kan wajecin kiyaye sulhu da zaman lafiya akasar a lokacin zabe.
Babban malamin addinin kirista na kasar shi ne ya kira jerin gwanon, inda ya ce suna goyon duk wani mataki da zai kawo zaman lafiya da kwanciyar hankali da fahimtar juna tsakanin al’ummar kasar.
A cikin wannan shekara dai za a gudanr da zaben shugaban kasa na farko baya kawar da gwamnatin Mugabe da ta gabata a kasar ta Zimbabwe.