Kamfanin dillancin labaran iqna ya habarta cewa, shafin yada labarai na Wasat ya bayar da rahoton cewa, magajin garin birnin Tripoli Abdulrauf Baitul Ml ya sheda wa manema labarai cwa,a daren jiya kawai iyalai kimanin 450 suka bar gidajensu domin tsira da rayukansu.
Y ace wannan na zuwa ne sakamaon hare-haren da dakarun Khalifa Haftar suke kaddamarwa ne kan al’ummar birnin na Tripoli da nufin kwace iko da shi.
Ya kara da cewa, yanzu haka wadannan iyalai suna zaune ne a cikin makarantu da kuma masallatai, domin rashin sanin makomar lamurra a birnin.