IQNA

An Hana Masu Kyamar Musulunci Yin Gangami A Kusa Da Masallatai A Holland

23:21 - September 05, 2019
Lambar Labari: 3484019
An hana masu tsananin kyamar addinin muslunci na kungiyar PEKIDA gudanar da duk wani gangami a kusa da masallatai a garin Ayndhon na kasar Holland.

Kamfanin dillancin labaran iqna ya nakalto daga shafin Datch News cewa, magajin garin birnin Ayndhon John Garitsma ya sanar a jiya cewa, babu wani wanda yake da hakkin yin gangami na nuna kyama a ga musulmia  kusa da wuraren ibadarsu.

Ya ce duk wanda yake son yin gangami domin bayyana wani ra’ayi nasa, to ya zo a gaban ofishin magajin garin birnin, domin hakan bai saba wa doka ba, amma yin gangami a gaban masallatan musulmi domin nuna rashin amincewa da akidarsu hakan ya sabawa doka.

Ya ce za su dauki dukaknin matakan da suka dace domin kare wuraren ibada na musulmi, tare da ladabtar da duk wanda ya sabawa wannan doka.

Kungiyar PEKIDA dai ta shahara a kasar Holland da ma wasu kasashen yankin wajen nuna tsananin kiyayya ga musulmi mazauna nahiyar turai.

3840225

 

 

 

 

 

captcha