Kamfanin dillancin labaran iqna ya habarta cewa, Saif badr kakakin ma’aikatar kiwon lafiya a lardin Karbala ya fadi yau cewa, mutane 31 ne suka rasa rayukansu, wasu kimanin 100 kuma suka jikakta a tirmutsitsin miliyoyin mutane da aka samu a yau a taron Ashura a Karbala.
Ya ce 10 daga cikin wadanda suka samu raunuka suna cikin mawuyacin hali, amma ana kula da su a asibitocin birnin.
Haka nan kuma ya yi ishara da cewa an samu tirmutsitsin ne a kofar Raja ta hubbaren Imam Hussain (AS) sakamakon yawan jama’a.