Kamfanin dillancin labaran iqna ya nakalto daga wasu majiyoyin Harka Islamiyya a Najeriya cewa, an gudana da janazar wasu daga cikin wadanda aka kashe a rana shura a kasar.
A ranar Ashura ta wannan shkara jami’an tsaron najeriya sun amfani da karfi a wasu garuuwan kasar wajen hana gudanar da jerin gwanon na magya bayan harka Islamiyya suke yi a kasar a kowace shekara, lamarin da ya yi sanadiyyar rasa rayukansu wasu daga cikin masu jerin gwanon, yayin da kuma a wasu garuruwan an yi an gama lami lafiya ba tare da jami’an tsaro sun taba kowa ba.
Tun kafin rana ta Ashura dai jami’an ‘yan sandan Najeriya sun fitar da sanarwa wadda a ciki suka yi gargadin cewa ba za su bari a gudanar da jerin gwanon na ranar ashura ba wanda magoya bayan harkar Islamiyya suke gudanarwa.