<?xml version="1.0" encoding="utf-8"?><rss version="2.0">
	<channel>
		<title>Labaran Kasa Da Kasa Kan Kur'ani</title>
		<link>http://www.iqna.ir</link>
        <description>IQNA,a Window to Spiritual World</description>
<item><title>An Yi Wa Wasu Daga cikin Kungiyoyi Da Cibiyoyi Rijista A Kasar Azarbaijan</title><link>/ha/news_detail.php?ProdID=946013</link><description>Bangaren kasa da kasa, an yi wa wasu daga cikin kungiyoyi da cibiyoyi na addini da ma wasu kadan da ba na addini ba rijista  akasar Azarbaijan a hankoron da gwamnatin kasar take yi na ganin cewa ta takaita da dama daga cikin ayyukan addinin muslunci a kasar.</description></item><item><title>Babban Burin Yahudawan Sahyuniya Shi Ne Haramta Ma Palaetiwa Hakkokinsu</title><link>/ha/news_detail.php?ProdID=946014</link><description>Bangaren kasa da kasa, jakadan jamhuriyar muslunci ta Iran a kasar Lebanon ya bayyana cewa babbar manufar yahudawan sahyuniya ita ce su ga sun raba al’ummar palastine da dukkanin hakkokinsu tare da mayar da su ‘yan gudun hijira baki daya.</description></item><item><title>Sanin Makomar Imam musa Sadr Na Daga Muhimman Abubuwa Ga Lebanon</title><link>/ha/news_detail.php?ProdID=946011</link><description>Bangaren kasa da kasa, daya daga muhimmanabubuwa da gwamnatin kasar Lebanon ta mayar da hankali kansu a halin shi ne sanin makomar Imam Musa Sadr a kasar Libya bayan da marigayi kanar Gaddafi ya sace shi tare da abokan tafiyarsa su biyu.</description></item><item><title>Yahudawan Sahyuniya Na Kira Da A Saki Tsohon Shugaban Masar Husni Mubarak</title><link>/ha/news_detail.php?ProdID=946012</link><description>Bangaren kasa da kasa, wasu daga cikin yahudawan sahyuniya sun fara yin kira da a saki Husni Mubarak tsohon shugaban mulkin kama karya na kasar Masar wanda yanzu haka yake fuskantar shari’a bisa zarginsa da kashe masu zanga-zangar lumana a kasar.</description></item><item><title>Baje Kolin Kur'ani Karo Na Shidda A Karbala Mai Taken Damunar Sakon Musulunci</title><link>/ha/news_detail.php?ProdID=945931</link><description>Bangaren kasa da kasa:a karo na shidda a garin karbala mai tsarki za a gudanar da taron baje kolin abubuwa da suka shafi kur'ani mai tsarki  da abubuwan addini da aka bawa taken rabi'ul Risala wato damunar sakon annabci  kuma ana gudanar das hi a daidai wannan lokaci na zagayowar ranekun tunawa da ranar haifuwar ma'aikin Allah tsira da amincin Allah ya tabbata a gare shi da kuma alayan gidansa da kuma Imam Jafar  Sadik (AS).</description></item><item><title>An Bude Ofishin Jigilar Musulmi A Jamus</title><link>/ha/news_detail.php?ProdID=945932</link><description>Bangaren kasa da kasa: a birnin Barlin na kasar Jamus da ke nahiyar turai an kaddamar da wani shiri mai matukar muhimmanci da zai rika yin jigilar musulmi da aka bawa sunan Taxin Musulmai da wani dan asalin kasar Iraki da ke zaune a birnin na Barlin ya kafa.</description></item><item><title>Yadda Suriya Ke Taimakawa Kungiyoyin Gwagwarmaya Ne Ke Bakantawa Manyan Kasashe</title><link>/ha/news_detail.php?ProdID=945933</link><description>Bangaren al'adu da fasaha: ofishin da ke kula da yada al'adun jamhuriyar musulunci a kasar Siriya ne ya bayyana cewa: kasar Suriya da gwamnatin kasar saboda dalilin tana goyan bayan kungiyoyin yan gwagwarmaya  ya ja mata yankwajini da karan zuka da kuma fuskantar fishin manyan kasashe ma'abuta girman kai a duniya da hadewa guri guda a kokarinsu na ganin sun ga bayanta .</description></item><item><title>Za A Raba Kur'anai Dubu Biyar Ga Masu Ziyara A Markadin Imam Rida (AS)</title><link>/ha/news_detail.php?ProdID=945934</link><description>Bangaren adabi:  babban darekta mai kula da harkokin hulda da jama'a a markadin Imam Rida (AS) ya bada labarin raba kur'anai dubu biyar   ga baki wadanda ba Iraniyawa da suka ziyarci wannan guri mai albarka a cikin kwanaki goma na alfijir din nasarar juyin juya halin musulunci .</description></item><item><title>Taro Kan Nasarar Masu Kishin Islama A Zabukan Kasashen Arewacin Afirka</title><link>/ha/news_detail.php?ProdID=944763</link><description>Kamfanin dilalncin labaran iqna ya habarta cewam, ya naklato daga shafin sadarwa na yanar gizo na pageshal cewa, za a gudanar da wani zaman taro kan nasarorin da masu kishin islam suka a zabukan da aka gudanar a kasashen da aka yi juyin juya hali a cikin arewacin nahiyar Afirka.</description></item><item><title>Gasar Karatun Hadisai Da Hardarsu A Birnin Nasiriyya Na Kasar Iraki</title><link>/ha/news_detail.php?ProdID=944766</link><description>Bangaren kasa da kasa, babbar cibiyar kula da harkokin kur’ani ta yankin Nasiriyya a kasar Iraki tare da hadin gwiwa da kamfanin diallncin labaran iqna za su gudanar da wani taro na gasar karatun hadisan iyalan gidan manzon Allah.</description></item></channel></rss>

