Kamfanin dillancin labaran iqna ya bayar da rahoton cewa, jaridar Daily Mail cewa, wannan zanga-zanga ta hada dukkanin bangarori na msuulm mazauna birnin.
A yayin jerin gwanon, musulmin sun rika rera taken yin tir da Allah wadai da harin da aka kai a birnin, tare da bayyana hakan a matsayin aikin ta’addanci da ba shi da wata alaka da addinin muslunci.
Kamr yadda kuma suka nuna jiyayinsu ga iyalan wadanda abin ya rutsa da su, musamman wadanda suka rasa rayukansu da uma wadanda suka samu raunuka.
A ranar Ahamis da ta gabata ce dai wani matashi dan asalin kasar Morocco ya kai hari da mota inda ya taka mutae tare da kashe wasu iamnin sha uku da kuma jikkata wasu fiye da dari.
Bayan hakan kuma ya fice daga motar ya tsere, amma daga bisani an gano matashin mai suna Yunus Abu Ya’akub dan shekaru 22 da haihuwa a wani wuri da ya boye a wajen birnin an Barclona, inda bayan dauki ba dadi daga karshe dai aka halaka shi.