IQNA

Wani Malamin Yahudawa Ya Tabbatar Da Cewa Suna Sayar da Makamai A Afrika

16:50 - January 09, 2018
Lambar Labari: 3482282
Bangaren kasa da kasa, Shalom Ainer wani malamin yahudawan sahyuniya a haramtacciyar kasar Isra'ila, ya bayyana cewa suna sayar da makamai a nahiyar Afirka.

 

Kamfanin dillancin labaran iqn aya habarta cewa ya nakalto daga shafin sadarwa na yanar gizo na arabi 21 cewa, wannan bayahude ya bayyana cewa sun jima suna gudanar da wannan aikia  cikin nahiyar Afirka.

Ya ci gaba da cewa, sayar da makamai yana da babar riba ga Isra'ila a dukkanin bangarori, kamar yadda kuma yake da muhimmanci a gare ta a siyasance.

Haka nan kuma ya yi isahara da cewa, cinikin makaman yakan shafi wasu gwamnatoci da kuma wasu kungiyoyin da suke fafutuka, daga ciki kuwa har da kasar Sudan ta kudu, inda suke sayar da makamai ga gwamnati da kuma wasu kungiyoyi a kasar.

Wannan malamin yahudawa ya kara da cewa, suna shirin ci gaba da kara fadada wanann kasuwanci na makamai a cikin nahiyar Afirka, inda lamarin zai hada da wasu kasashen da ba su shiga cikin shirin ba a lokutan baya.

Abin tuni dais hi ne haramtacciyar kasar Isra'ila ta jima tana sayar da makamai a cikin nahiyar Afirka, musamman ma ga kungiyoyin da suke tayar da kayar baya ga gwamnatoci a cikin kasashensu.

3680508

 

 

 

captcha